Tuesday 13 December 2016

FAKON NUMFASHI COMPLETE

Phakon Numphashi

Written by MRS SAIF
Kai❗gaskia piracy bai yi ba,haba jama'a ya xa a yi mutum ya dage ya xuba idean sa ya sha wahalan typing wani gardi ko gardiya su kwashe,wato su yi editing su cire sunanki su saka nasu,a xaton su sun ci bilis toh ku kwana da shirin duk abinda mtm yayi walo khairan ko sharran sai Allah ya tambayeku akai.
Kuma addu'ar wanda aka xalunta kar6a66iyace,bani na fada ahe
Kuma duk wanda ya mun edting novel sai dai nace sai mun hadu a gaban Allah don ba yapewa xan yi ba.
Amma ban da wa'en da suke hada mana buks din mu wuri daya idan da gyara ma wasu kan gyara ba tare da sun cire sunanka ba.Wannan se dai mu jinjina muku

1***
Kallo daya xaka yi masa ka tabbatar da irin 6acn ran da yake ck,gava daya idanunsa sun kada sun yi jawur tamkar gauta,annurin puskarsa ya dauke tamkr bai ta6a dry ba,gashn jknsa ya mimiqe, sai huce yake yi yana purxar da wata xaxxapar iska,gaba daya xuciyar shi a cunkushe take da tari baqin ciki,sai wani irin bugu take yi tamkar xata keta qirjinshi ta fito.

Sai safa da marwa yake yi ackn kataparen parlon nasa,duk da sanyin ac da ya game ko'ina na parlon amma gummi yake kamar an watsa masa ruwa tsabagen bacn ran da yake ciki.

Dattijo ne mai kimanin 65-70yrs a duniya,amma idan ba an fada ba,ba xaka ta6a cewa ya kai shekarun ba.savoda hutu da jindadi sun ratsa shi ta ko'ina.idan banda yanxu da yake ckin tashn hnkli a daliln er ciknsa.
             
             
Maman Twins


phakon Numphashi

Written by
    MRS SAIF

2***
A gefe kuma wata tsaleliyar budurwa ce wadda va xata wuce 22yrs a duniya ba,tana durqushe a gabansa tamkar xata kifa savoda tsoro da fargabar halin da ta tsince kanta a ciki,gava daya jikinta rawa yake yi tamkar maxari.

Cikin dashashshiyar muryarta mai nuni da cewa taci kuka har ta gaji ta para magana"tace wallahi abi ban aikata abinda ka............dif ta dauke wuta sakamakon tsawa da ya dakaa mata,savoda tsoran da taji har sai da ta kipa ta buga kanta da karpen daya dg ckn stools din dake parlon,ba shiri ta dape kanta tare da sakin wani kuka mai ban tausayi.

             
Maman Twins
Phakon Numphashi

Written by
              MRS SAIF
3***
Ummy ce tashigo da sauri tana padin"lafiya?mai ya paru ne AFIF❓irin wannan kuka kamar an yi mutuea.Abu thauban mai yake faru ne??? Ta juya tana duban m.gidan nata,
A jiyar xuciya yayi tare da miqa mata wata parar takardar dake hannunsa.yana padin"duba ki ga sakamakon tasts da aka yi mata.
Kar6a ta yi tabi tests din da kallo daya bayan daya,daga qarshe idonta ya dire akan PT da aka yi mata.
Dam!dam!!dam!!! Ta ji xuciyarta na tsananin bugawa,domin gani tayi PT positive.

Hankalinta yayi matuqar tashi,amma sai tayi qoqarin dannewa don tasan halin shi sarai akan aqidarsa.
Tace"abu thauban ban gane ba???
Juyowa yayi ga dubansa gareta yace kamar yaya???sai kace ba ki iya krtu va,ga abu nan baro2,kice ba ki gane va.

Tace" na gani a rubuce amma kana nufin ka yarda Afif tana da ciki❓Bayan kasan wacece Afif ciki ta waje,kasan irin tarbiyar da muka bata,kuma bata xuwa ko'ina sai da body guards,bata da qawaye,bata kula samari sam-sam,duk haukan da samari ke yi kanta mu shaidane bata sauraransu.
Saurayi daya ne tak take kulawa kuma da amincewarka ko nace ma xa6inka ne.
Yau kuma kusan 6mnth baya qasar gava daya bare ace shine,tunda result ya nuna cikin na 8wks ne.

               
Maman Twins



phakon Numphashi

Written by
            MRS SAIF

4**

A xafafe ya daga mata hannu yana cewa"dan yau ana shaidasa ne,ki kalli irin tarbiya da kulawa da na bata amma daga qarshe shine ta watsa mun qasa a ido.
Juyawa da dubansa wurin Afif yayi yana cewa"na dauki tsawon shekara ashirin har da biyu ina tarbiyyantar dake,na dauki dukkan kulawata na dora akanki,inata kaffa-kaffa dake,inata ririta rayuwarki,domin dai na samu na aurar dake lpy ,kema ki xama uwa tagari ga 'ya'yanki.
Amma abinda bai kai shekara wannan burin nawa ya cika va,sai ga shi kin wofantar da tarbiyyar dana baki kin wulaqanta rayuki,amma kanki ki............wani irin tari ya tarnaqe shi ya kasa qarasa maganar ya durqushe a gurin.

A hanxarce Afif tayi kansa da niyyar ta riqeshi;yayi mata nuni da kada ta sake taxo inda yake,ba shiri ta koma da baya hawaye na ambaliya a puskarta.
Tana tunanin yanxu itace silar shigar da Abynta wannan halin ,bacin tsantsar qauna da ya nuna mata.........
Tana ckn tunanin ta ji ya fara magna"ki sani daga sai yau bani ke,babu abinda xai kuma hada ki da xuri'ata.
Baxa ki koma xama a gidan nan ba,ki je can ki qarasa lalacewarki,kuma ban yarda ko kadan ki je wurin dangi na va.

                 
Maman Twins




phakon Numphashi

Written by
              MRS SAIF

5**

Cikin tashin hankali ummy ta rusuna a gabansa tana"fadin Abu thauban wannan hkuncn yayi tsauri da yawa don Allah a sassauta mata.
Ko kallon inda take bai yi ba,sai tsawa da ya dakawa Afif tare da padin"xaki tashi ki fice ko sai na saka an xo an yi waje da ke???
Kukan Afif ya tsananta sosai,cikin kuka take fadin Aby wallahi bansan komai ba akan wannan lamarin ba,ban aikata abinda kake xargina da shi ba.

Ummy ma tasowa tayi tana kuka ta rungumeta tana cewa"tabbas Afif akwai wani 6oyayyan al'amari tare da ke.
Haba Abu sauban baka tunanin ko an hada baki da dr yazeed don 6atawa Afiif suna❓kuma don kaima ya shapi siyasar ka❓
Cikin dacn rai ya fara magana ta yaya dr yaxeed xai mun qarya sama da shekara 10 muna tare bai ta6a yi ba sai yau???
Xaki saketa ta tafi ko sai nayi mugun sa6a miki.
Afif da sauri ta xare jikinta daga na ummy tayi hanyar pita gudun abinda xai je ya xo.Don tasan halin Abynta kaifi daya ne idan yace a to baya ta6a komawa yace a'a.
Kuma baxa ta so matsalanta ya shapi auren iyayenta ba.
A bakin qofar pita ta tsaya tana padin"Aby da ummy ku yape mun kuma ku yarda dani ban taba aikata abinda ba kwaso ba,tana kuka tana padin Aby wallahi ban taba kusantar xina ba balle har na aikata ta,
Ummy don Allah ko na tafi ki qara bawa aby hakuri,ban yi abinda yake xato ba,ban yi ba.........   ban yi ba ............kuka yaci qarpinta ta pice da sauri bata jira abinda ummy xata ce ba.

               
Maman Twins


Written by
                 MRS SAIF

6***

Ummy da sauri ta tashi domin binta,aby ya dakatar da ita tare da padin"idan kk sake kk qara wani taku da niyyar binta,to a bakn aurnki.
Ummy dai suman tsayae tayi domin runda syke da shi bai ta6a gigin fadin makamanciyar wannan magnar ba.
Kaitsaye dakinta ta shige don wani irn ciwo ta ji kanta na mata ga zazza6i na shirin rufeta,ba shiri ta haye kan gado ta qudundune da bargo.

Afif na futowa get din gidan ta nufa,guards din dake gurin suka bita da kallo,ko kallnsu ba ta yi ba ta wuce,da sauri body guards nata suka biyota,suna fadin ina xamu ne ranki ya dade???bata kula su ba,bare su sa ran xata yi musu magna,ta cigaba da tapiya abinta.
Can kuma taji kmr sun daina binta,babbansu yana waya da alama aby ne ya kira,taji yana cewa"ok sir angama.
Ko ban tamvaya nasan aby cewa yayi kar su biyo ni.

Da sauri na qarasa fita dg ckn gdan,na tsaya awaje ina qarewa gidan kallo.Ina share hawayn da ya kasa tsaya dg idona,ina tunanin na bar gidanmu,gidan iyayena kuma mahaifata.
To yanxu ina nufa??kunma wace irn rayuwa xan tsinci kaina nan gaba❓shin ta yaya na samu ciki❓bayan nasan a rayuwta wani namiji bai ta6a kusanta ta ba.ko ana samun ciki hk kurum........

                 
Maman Twins


Phakon Numphashi

Written by
                 MRS SAF

7***
Innalillahi wa'innailaihirraji'un ta iya fada ta durqushe a gurin ta saki wani irin kuka mai tsuma xuciya.
Sai da ta ci kukanta mai isarta,ko kare bai gifta ba,kasancewar unguear tasu ba mtne sosai,domin unguwace ta manyan qasa.
Ta tafiya ta para ckn tsoro da fargaba don dare ya para yi tunda tuni anyi sallr magrib,tunda take bata ta6a pitowa a qasa ba kuma ita kadai sai yau.
Gashi wurin vabu alamar xata samu abin hawa na hayab duk sai motcn gida.Tun tana tapiya tana iya daurewa har ta kasa,ta nemi can gefen titi ta xauna irin gurin da ake saka interlock.
Kawai sai ta saki kuka mai ban tausayi,tana tnanin ina ta nufa da daddaren nan,amma ta dauki alwashin baxa ta kuma kwana a garin abuja ba,gwanda tayi nesa da garin ko xata samu sassauci.
Sai dai wani garin xan je??tambyr da ta jefawa kanta kenan.
Ko maiduguri kawai xanje,sai kuma can tace ko kaduna xan je ne??kai gaskiya kd tayi kusa,kawai bari na tsaya a kano ta dabo.

Tana gama yanke shawara kuma sai ta ji wasu xafafan hawaye na biyo kumatunta,don bata san ta yaya ma xata je kanon ba,tashar da ake xuea a shiga mota ma va ta sani ba,idan ma ta sani da wani kudin xa ta je❓
Tuni wani kuka ya qwace mata ta cusa kanta cikn cinyoyinta ta cigaba da rerewa.

             
Maman Twins


Phakon Numphashi

Written by
                 MRS SAIF

8***

Tana ckin wannan halin sai ji tayi an haske mata ido da fitiln mota,a raxane ta dago kanta don gani waye.
Wata budurwa ta gani da bata wuce sa'arta ba ta pito dg motar tana padin"baiwar Allah lafya kika xo nan kika xauna da da daddaren nan???
Sai kuma tabi ta da kallo tana fadin ni kmr ma na sanki???
Afiif da sauri ta girgixa kanta tace"gaskiya bani bace.
Tace"ok;ina ganin kama ce kawai.
Ni suna na Nuhailat Abba Nasidi,abun da yasa na tsaya;tun daxu da na wuce na ganki anan wurin a xaune,kuma har na dawo duk kina wajen.
Na dauka ko 6ata kk yi shiyasa na tsaya don na taimaka mk.

Domin gaskiya a matsayinki na 'ya mace bai kamata ki xauna anan ke kadai ba,domin kinsan duniya ba gaskia yanxu.
Idan vaxa ki damu ba ko xa ki iya gaya mn damuwarki???
Afif kukanta ta cigava da yi kawai,kafadanta ta dapa sannan tace"ban tsaya nan don na cutar dake va,sai don na taimaka mk don bana son na ga dan uwana musulim a ckin wani hali van taimaka masa ba,matuqar ina da halin yin haka.
Juyowa tayi da kallonta xuwa ga yarinyar da ta kira sunanta da nuhailat,tace"don Allah taimako daya nake son ki mun,ki kai ni tasha.
Cikin xaro idoNuhailat tace"tasha wurin me???

       
     
Maman Twins


Phakon Numphashi

Written by
                 MRS SAIF

9***

Afif tace"kano xan je,dama ke er kano ce???cewar nuhailat,a'a.
To mai xaki yi a kanon???Afif ta fara gjiya da tamvayoyin nata,sai tace"kawai can nake son xuea.
Nuhailat ta gama gane damuea ce tayi mata dabaibayi,savoda hk tace da ita ta shigo su tafi.
Domn Allah ya sani baxa ta iya tafiya ta barta a gurin ba.don akwaita da tausayi.
Sai da suka hau kan titi,saannan ta dubi Afiif tace "ya sunanki ne??
Suna na Afiif tace da ita,Nuhailat maimaita sunan tayi a ranta,anya kuwa ba ta san yarinyar nan ba???
Sai da suka yi nisa a tapiya tace"Afif da xaki bi shawarata da kin haqura da tafiyarnan har gobe da safe,tunda kin ga yanxu har taran daere ya wuce.
Vari ma na tambayeki,wai 6ata kika yi ko me???
Afif shiru tayi tana tunanin me xata ce mata,don gaskia vaxa ta iya gaya mata ainihin abin da ya rabota da gida ba.
Kawai ta kaita tasha ta shiga mota don yanxu bata jin tsoron mutuea kwata2 gwanda ma ta mutu ta huta da wannan halin da take ciki.

       
     
Maman Twins
Phakon Numphashi

Written by
                MRS SAIF
10***

Sai da nuhailat ta maimaita a karo na biyu,sannan ta fara magna"a 6ata na yi ban gane gidan da naxo bane.
Ok,to ki gaya mun address sai mu bincika ko xa mu samu.
Ckn inda2 Afif ta para magna........ai na ...........na rasa kayana duka har wayata,a inda na tsaya cin abinci aka sace mun.
Ayyah!!!nuhailat ta fada,shikenan sai mu wuce gidan mu gobe da safa sai a kaiki tasha ki shiga mota.
Afif tace"to na gode.
Suna shiga gidan kaitsaye bangarenta ta kai afif,ta nuna mata toilet tace ta shiga tayi wanka tayi sallah.ita xata je ta yiwa mummynsu bayani dg nan ta sa a kawo mata abinci.

Tunda safe Afif ta shirya jira kawai take ace ta pito akaita tasha,domin yanxu gaba1 garin ya pice mt a rai.
Yau ga shi ta kwana a garin abj ba a gidan iyayenta ba.
Wasu xafafan hawaye ta ji sun sauko akan kumatunta.
Nuhailat ce ta shigo tana fadin"wai ke ba kya gajiya da kuka ne???
Don Allah ki yi haquri duk da naga bakya son padin damuwarki,amma komai yayi xafi maganinsa Allah.
Ga shi mummy ta baki 10k ki shiga mota,ki pito driver na jiranki.
Afif tace"ta gode Allah ya saka da alkhairi.

               
Maman Twins


Phakon Numphashi
                  MRS SAIF

11***
Bayan sun tafi nuhailat har kuka tayi don dan xaman da suka yi Afif ta shiga ranta.
Tunda ta shiga mota take aikin kuka,domin rashn sanin takamanmen inda ta nufa.
Har wata mata dake xaune kusa da ita ta pahimce tana cikin damuwa,ta tausaya mata duk da bata san damuwarta ba.
Tace"da ita sannu.
Afif ta dago da kumburarrun idanunta tace"yawwa.
Matar tace"don Allah kiyi hquri ki daina kukan nan hk kar ya saka miki wani ciwon kin ji.
Afif daga kanta tayi tare da qoqarin share hawayn dake ambaliya a idonta.
Da hk matar ta riqa janta da hira don dai ta samu ta rage mata damuwa.amma ta kasa sakewa da ita don damuwar dake cin ranta.sai dai jefi2 ta kanyi wasa da yarinyar dake hannunta.


Da hk har sk shigo garin kano,ana xuwa na'ibawa matar tace"xata sauka,sai afif ta tsince kanta da shiga damuwa don tana tunanin idan sunka atasha ita wace unguwar ta nufa???
Sai tace itama a sauketa anan.
Matar ta juyo tayi murmushi tace"kema anan xaki sauka ashe.???tace eh.
Matar Tace"ok ni kin ga ina tsallakawa sai gida.
Afif kawai sai tabi matar sai da suka tsallaka titi,matar tace"ashe kema anan hk kike???

Afif ba tace komai ba illah hawaye dake bin fuskarta.
Matar tace wai meke faruwa dake ne tun dg abj har kano kk kuka ko ba ki gane inda xaki ba ne❓


             
Maman Twins


Phakon Numphashi

          MRS SAIF

13**
Daga kai kawai ta yi alamar a,matar ta sauke a jiyar xuciya domin dai yarinyar hk kawai tausayi take bata.
Tace"yanxu mu qarasa gidana ma yi magna,don tsaya a hanyar ba shi da amfani.
Ba musu Afif ta bita.

Gida ne madaidaici,mai dauke da dakuna 3 sai kitchen,store,da toilet.
Bayan sunyi sallah sun ci abinci,matar tace da afif ta gaya mata sunan unguwar da ta xo,duk da mijinta baya nan sai su je da kansu su bincika.

Afif ba magna sai kuka,matar tsayawa tayi tana kallnta don akwai ayar tmbaya akanta.
Wace irin tafiya ce wannan tayi daga ita sai kayan jikinta,kuma da an mata magana sai kuka,ga yarinyar a wani firgice.

               
Maman Twins

Written by
                 MRS SAIF

1 4 **
*komawa tayi ta xauna inda afif take,ta dago da puskarta,
Tace ya sunanki ne???
Afif tace da ita.
To ni kuma suna na Suhaima.
Nan muka xo gidana ne,mijina ba'a garin nan yake aiki ba,yana kwara state,ina da yara 2,kin ga daya,dayan kuma na bar shi anan yana gidanmu savoda school ban je da shi.
Naje abj.bikin wata cousn dina,a hanyata ta dawowa mk hadu.
Ina fatan kin gamsu da bayani na.
So ki daure ki sanar dani lbrinki don nasan ta yadda xan taimaka miki.
Don na fahimci akwai damuwa atare da ke.


Sassauta kukan tayi tare da fadin"xan sanar dake gaskiyar labarina,Aunty suhaima,ko xan samu ki tausaya mn ki sakani a haske domin yanxu duhu ne ya gama mamaye ni ta ko'ina.

Suhaima ta dafata tace"ki daina kuka Afif ya isah,sanar da ni ina jinki.



               
Maman Twins




Phakon Numphashi


             MRS SAIF

15***

Da farko dai suna na AFIF NASIR MAINASARA,Mahaifina bafulatanin gombe ne.,Currently senator ne a garin gomben,mahaifiyata kuwa balarabiyar Oman ce.

Mu 5 ne ras agurin iyayen mu akwai:yaya thauban,yaya sabit,yaya sabir,sai yaya abid da nake bi.
Nice auta agidanmu,kuma ni daya ce mace kwal,saboda hk iyayena suka dauki son duniya da kulawa suka dora akaina.

Duk da mahaifina hamshaqin dan siyasa ne,don kafin ya xama senator ya taka matakan siyasa da dama,yanxu hk xuwansa majalisa 2 na uku xai yi,daga nan yana da permanent seat a majalisa.
Amma hakan bai hana shi jajircewa akan tarbiyar mu,don shi mtm ne kaifi daya.
Duk da kalln da ake yuwa en siyasa na rashn gskia da amana,maganar gaskia mahaifinmu ba hk yake ba,don ba duka aka taru aka xama daya va.
Aby kam yana samun yabo ta kowacce fuska,don talakawan da yake wakilta suna jin dadin wakilcinsa.

Mutum ne shi mai gaskia,kuma yana tsayawa akan haqqin talakawa.
Don dai yana da wadataccen ilimin addini don mahaifinsu shahareren mlmin addini ne alkcn da yana raye.


               
Maman Twins




phakon Numphashi

Written by

               MRS SAIF

16***

Babban wanmu,thauban yayi karatunsa ya gama har ya fara aiki duk a qasar thailand.
Yana da mata, da da daya.

Sai mai bin sa Sabit shima ya gama karatunsa ya fara aiki a NNPC yana PH,shi da matarsa.

Sai Sabir da Abid su kuma suna england wurin baffa sulaiman qanin Abynmu.

Ni kam tun da na dira a duniya iyayena da duk wanda ya ra6e mu ake nunamin tsananin qauna.
Tun ina jaririya kyawuna baya 6oyuwa duk irin jinsin da na shiga,takanas mutane ke xuwa gidanmu don kallona.
Don kuwa ance.........hmmm ai nima shaida ce Afif aunty suhaima ta katseta,sannan taci gava da fadin"don lkcn da muka hadu ban ta6a tunaninn ki na jin hausa ba,don gwada ce miki sannu na yi.Sai na ji kin amsa.

Don ni kam arayuwata ban taba ganin kyakyawa kamarki ba.
Savoda xaki ga ana kwatanta kyawawa da jaruman fina2,musamman na india,gaskia ke ban ga wadda xan kwatanta kyanta da na ki ba.
Ko ke don ruwa biyu ce ???
Sai kyan naki ya xama wani special.
Xa a iya kiranki da doguwa,amma ba xanqalqal va,baki da qiba sosai amma baxa a saka ki a layin ramammu va,structure naki yana da masifar kyau nd ur voice tamkar ana busa sarewa.

Farar fatarki sak ta larabawa,gashin kuwa xan iya kwatantashi da na indiyawa cox yana da tsawo daa tsantsi kuma ga shi black wuleek.


             
Maman Twins



Phakon Numphashi

         MRS SAIF

17***

Babban abinda ya kuma qawata fuskarki shine:dara-daran idonki masu dauki da wani sirri na xaiba da ya xagaye dukkan baqin dake cikin idonki.


Gskia Afif kyanki na daban ne,sai dai nace masha'Allah.
Afif murmushi tayi tace"ka ji aunty suhaima.
Suhaima tace"yoo ai maganar gaskia ce, ni dai cigava.
Tun ina qaramata na taso da wani irin farin jini duk inda na shiga sai na fito da kyaututtuka na jama'a.

Aby yana matuqar sona don yana son 'ya'ya mata,ko don ba shi dasu da yawa ne.
Tun da na gama pri sch.ummy taso na pita waje karatu kmr yadda sau en uwana su kayi.
Amma qememe Aby ya hana yace"baya son na yi nesa da su.

Ko da na gama sec sch.da kyar ya amince,amma yace"sai dai na je Oman qasar su ummy don can xa'a fi kula da ni.


Tun kafin na gama sec sch;samari tamkar xa su yi hauka akaina,Aby  ga abin yayi yawa;ya hada ni da body guards duk inda xan je muna tare,islamiyya ne kawai nake xuwa ni kadai.


Akwai wani kabeer yanda kika san maye hk yake,duk matakan tsaron da aka saka akaina,amma duk wani motsi na wa ya sani,idan yau na yi niyyar xuwa wani guri xaki gansa agurin.
Koda ba xai yi mun magana va;kawai shi dai ya kalleni ya tafi,
Na rasa wake sanar da shi.

Nan da nan aka nema mun addmssn a Oman. karatu ma dadi nake yi.
Tunda duk inda na juya acikin dangin ummyna nake.


           
Maman Twins
Phakon Numphashi

Written by
          MRS SAIF

18***
Kafin na gama makaranta na hadu da wani saurayi,mai suna Aufiq dan asalin qasar Oman ne,Allah ya hada jininmu sosai,don yana masifar sona,nima ina son sa don yana da halaye masu kyau.


Gashi kyakkyawa first class don mutane da dama sun dauka dan uwana ne,don ance muna kama.

Ashe ma dan aminin Aby ne,xaman da yayi a qasar kafin ya auri ummynmu suka yi matuqar shaquwa.
Kuma ko da ya koma 9ja ba su daina xumunci va.

Lokacin da iyayen mu suka ji tsakaninmu va qaramin farin ciki suka yi ba.
Don dama sun yi maganar hada mu aure,sai ga shi faduwa taxo dai2 da xama.

Na gama karatu na cikin nasara na dawo 9ja cike da jindadi,kowa na gidanmu ya taya ni murna.
Aby ya hada mum kwarya-kwaryar walima don taya ni murna.
Haka ya saka en uwana duk su xo,da en uwansa dake gombe duk sun hallara.don taya nu murna.


             
Maman Twins




Phakon Numphashi

MRS SAIF

19**

Bayan an gama hidimar walima kowa ya watse,Aby ke sanar dani da ya so asaka bikinmu a wannan shkrar,amma yanxu ba hali,saboda an tura Aufiq course, va qasar spain sai dai dan ya gama.

Tunda na dawo dg Oman bana xuwa ko ina,ina gida;da xaman gidan ya isheni nace"da aby xan koma islmiyya bai yi musu ba,don shima akwai shi da son karatu.

Ban dade da komawa ba;aka kawo mana wani sabon malami wai xai riqa koya mana tajweed.
Kinsan wa na gani???
Aunty suhaima tace"a'a
Kabeer ne wannan nataccen saurayin da nake gaya miki.
Nayi mamaki don ban ta6a tunanin yana da ilimin islama ba,don ya pi kama da dan boko tsantsa.

Kuma nasan babansa baabba ne aqasar nan,to mai ya kawo shi teaching???
Kuma a islamic school.
Duk da dai makarantar baabba ce kuma ana ji da ita a garin abuja.


           
Maman Twins





Phakon Numphashi

MRS SAIF

20***

Lkcn da ya fara koyarda mu na sha mmki domin yasan aikinsa,idan kin ji yadda yake fitar da makharijul huruf sai kin yi mamaki don ku ni da na shafi larabawan sai hk.

Duk yanda yayi ya kulani bana ba shi fuska,don ko alamar na ta6a saninsa bana nunawa.


Na samu kusan 4mnth da dawo wa,kwatsan wata rana sai na tashi da xaxxa6i da ciwon kai,daga baya kuma sai amai.

Hankalin iyayena yayi matuqar tashi,domin Aby baya son gani na cikin wani yanayi kwata2.
Nan da nan yayi wa family doctornmu waya(dr yaxeed)
Ba da dadewa ba ya xo,ya hau yimun gwaje2 har fitsarina ya dauka.

Washe gari da sassafe ya kawowa Aby black result din da ya tarwatsa farin cikin rayuwata,ya tarwatsa nagartaccen tubalin da ya ginu tsakanina da iyayena................kuma shine sanadiyyar.......................wani irin kuka Afif take yi tamkar ranta xai fita
Kukan ne ya tilas ta mata yin shiru ta kasa qarasa ba mu lbrin.

Sai nace"ku biyo ni da xarar Afif ta samu nutsuwa xan cigava da dauko muku rahoto.

       
        👎
Maman Twuns
[22:02, 07/01/2016] Phakon Numphasho

Written by

                MRS SAIF


Aunty suhaima kanta kukan take yi,da kyar ta saita kanta,sannan ta rugume Afif tana fadin"
Ki yi haquri afif,rayuwa ce kowa da yadda take xuwar masa.
Wannan kukn ya isa hk,kada ya saka miki wani ciwon.

Da kyr aunty suhaima ta shawo kanta,sannan ta cigava da fada mata yadda suka rabu da iyayenta,har xuwa haduwarsu da su haiman.

Aunty suhaima jinjina kai kawai take,sai can kuma tace" da afif,
ki gaya mun tsakani da Allah ba ki ta6a ke6ancewa da wani namiji ba❓

               
Maman Twins


Phakon Numphashi

MRS SAIF

22***

 domin fadar gaskiar ki ga reni shi xai saka na san matakin da xan dauka akan lamarin.

Cikin kuka afif take fadin"ban ta6a tun da nake,ko hannu na,na miji bai ta6a riqewa va.
Aunty suhaima fa gaba daya kanta ya kunce,wannan wani irin al'amari ne,tabbas ta yadda da maganar yarinyar,don yanayinta shi ke qara gasganta maganarta.

To ko dai an hada baki da dr yaxeed ne,kamar yadda ummynki ta fada.
Ban sa ni ba,nima abinda nake son na gano kenan,ta yaya xanyi ciki va tare da sani na ba❓❓

Kawai yanxu abinda xa'a yi ki shirya mu je asibiti,dole acan xa'a tabbatar mana da gaskiyar lamarin.

Kaitsaye wani private hospital su ka je,anan kusa dasu don akwai qawar aunty suhaima dake aiki a gurin.

Sun ci sa'a kuwa tana nan,ba tare da 6ata lkci ba a.suhaima ta sanarda ita abinda ya kawo su.
Tace"ai ko kun ci sa'a babban likitnmu yana nan,yanxu hk scaining yake yi,sai ku biya kudin kawai a mata.

Dmn yin hakan shi xai fi tabvatar muku da abinda kk xargi ko rashinsa.
Nan da nan sk biya, afif ta shiga gurin scain.bayan an gama dr yace"ta jira a waje xai turo nurse ta kawo musu result.


               
Maman Twins



Phakon Numphashi

MRS SAIF


23***

Suna nan xaune,sai ga qawar aunty suhaima ta pito daga office din dr tare da wata farar takarda a hannunta.

Tunkan ta qaraso gaban Afiif ke dukan uku2.
Tace"gaskia Suhaima yarinyar nan tana da ciki,har na tsawon 8wks 2dys, haka result ya nuna,tare da miqa mata takardar.


Ai ba afif va,har suhaima gabanta dukan tara2 ya riqa yi.
Haka suka yi sallama da nurse din suka dawo gida,jiki ba kwari.

Bayan sun dawo gida Afif ta fashe da wani irin kuka,tana fadin"a.suhaima don Allah ki ga ya mun ta yaya ake samun ciki???
Haka kurum ciki yana pitowa a jikin mut❓❓


         
Maman Twins




Phakon Numphashi

    MRS SAIF


24***
Aunty suhaima ita ma kukan take yi sosai,tace"tabbas afif ciki va ya pitowa hk kurum,sai dai inda akwai wani 6oyayyyen al'amari a tare da ke.
Wanda ke kanki ba ki san da shi va.

Islamically,Allah (SWA) yakan hallice dan adam ne ta hanyar haduwar jinsi biyu(mace da namiji)idan kika cire mutum 3 ga su kamar haka"

1Annabi Adam(AS) Allah ya halicce shi ba uwa ba uba.

2 Nana Hauwa'u ita kuma Allah ya halicceta da uba,amma ba uwa.

3 Annabi Isah(AS) shi kuma Allah(SWA) ya halicce shi da uwa,amma babu ubah.

Wannan duk hukunci ne ubangiji,don ya ishemu ishara,mu san babu abinda ya gagari Allah(SWA)


Sannan addinin islama bai nuna mana akwai wanda xa a kuma haifa nan gava babu uba va.
Dole sai da uba,saboda hk Afif akwai dai abin da ya faru dake.
Da
Sai dai mu ce"Allah ya bayyana mana ko meye.



           
Maman Twins





              25***

Kuma na mk alqawarin xama tare da ke har xuwa lkcn da iyayenki xa su neme ki da kansu.

Yau kusan 4wks kenan da xuwanta gidan,xaman su suke yi tamkar uwa daya uba daya,tana tausayawa afif,tana kula da ita,duk abinda take buqata aunty suhaima na qoqarin ba ta.

Hatta kayan sawarta bayarwa take yi ana wanke mata,domin tun xuwanta ta debo mata ackn nata,sannan ta bayar aka dinka mata wasu.

Ba laifi afif tana samun nutsuwa ta hanyar suhaima.
Afif na kwance a dakinta ta ji ana ta kwada sallama.
Fitowa tayi tana ta fadin"waye??
Kasancewar a.suhaima bata nan ta je dauko yaranta daga sch.
Shigowa ta yi ta bi Afif da kallo tana fadin"ina matar gidan ne???
Afif tace"Ba ta nan.
Matar tace"idan taxo kice makociyrta ce Rabi ta xo.
Afif tace"toh.


             
Maman Twins




Phakon Numphashi

             MRS SAIF

26***

Bayan aunty suhaima ta dawo,sai ga matar ta kuma dawowa,suna shiga parlor ko xama ba tayi va ta hau rambayar A.suhaima"
Wai waccen balarabiyar ina kuka samota???
A.suhaima tace"qanwata ce.
A haba!!! Kwata2 amma ba kwa kama???
Da ganin waccen prettyn sai dai jinsin arab ko india.
A.suhaima tace"ai qanwa ba sai lallai d same mum & dad,akwai ta dangi ai.

Matar gyara xama tayi tace"yanxu kina nufin er dangi ce kike xaune da ita,wannan kyakkyawar yarinyar.

Ai ni fatan da nake Allah ya sa har ta gama xamanta a unguwar nan kar ta hadu da mijina,domin ko mace ta kalleta dole ta kuma kallonta bare kuma namiji.

Aunty suhaima tace"ai ke rabi kishinki na daban ne,tayaya xata hadu da mijinki???
Vayan yarinyar da tun da taxo ko qofar gida bata fita.

To ai dole nayi addu'a domin akwai 6acin rana.
Ke ma don mijinki baya gari ne,amma shawarar da xan ba ki.
Ki sallame ta tun kafin ya dawo.

             




Phakon Numphashi


         MRS SAIF

27***
Murmushi A.suhaima tayi tace"toh.
Don idan ta nuna bata dauka ba,ta riqa damunta kenan akan xancen.

Amma duk da haka duk ranar da suka hadu sai ta yi ta xuga aunty suhaima akan ta kori afif,ita kam bata dauka don tasan taimako take yi savoda Allah.


Yau kam gidan sun tashi sai shirye2 suke na taron mai gidan.
Tun qarfe 2pm suka gama abinda suke yi tsaf.
Aunty suhaima kaitsaye wanka ta shiga.
Afif kuwa daki ta wuce bayan tayi sallah tabi lfyr gado domin ta gaji abinka da mai ciki.

Qarfe 4:30 ya shigo gidan yaransa suka ruqunqumeshi suna fadin"Abba oyoyo!!!
Aunty suhaima ma dai sahun en oyoyon ta bi.

Afif kuwa tana chan tana shaqar barcnta da gudu bilal ya haye kan gadon yana fadin"auntie afif ki xo Abba ya dawo.
Tace "toh jeka ga ni nan xuwa.
Yace"to sannan ya fice dg dakin.
Yana fita ta ja vargo ta cigava da barcnta,don bacci ne a idonta sosai.

Sai wurin 5:15 aunty suhaima ta shiga dakin Afif tana fadin;wani irin barci ne kk yi hakaa,har an yi sallar la'asar tun tuni.
Miqewa tayi tana cewa"ni kaina bansan wani irin barci nake yi ba yau.


                 👎
Maman Twins😍
[22:02, 07/01/2016] Umma k: 🙆Phakon Numphashi😭

Written by
                MRS SAIF

2⃣8⃣
Aunty suhaima tace"sai ki tashi ki je ki yi sallah;sannan ki je ku gaisa da Abbansu bilal.
Afif tace"toh
Sannan ta fice daga dakin.


Cikin sallama ta shiga parlorn,dagowar da xai yi idanunsa suka yi toxali da kyakkyawar fuskarta.

Sai gaishe shi take yi amma bai san ma tana yi ba,sai da aunty suhaima ta dan xungure shi tace"
Ana gaisheka fa.

A diriri ce yace"na........am.....eh....toh......lfy.Daga nan Afif bata kuma cewa komai ba ta fita.

Da xata fitan ma binta yayi da kallo,har sai da A.suhaima ta kalleshi,sannan ya wayance yana sosa qeya.


Sageer dai tunda ya dora idonsa akan Afif ya kasa samun sukuni,ba shida wani tunani sai nata.
Ya dau alwashin sai ya cika burinsa akan Afif ko ta halin qaqa.

Ita kam Afif gaba daya ta takura agidan tunda ta fuskanci irin nacin kallon da sageer ke mata.
Ba dama su hadu sai ya riqa wani kashe mata ido,kuma ko kunyar aunty suhaima baya ji,don ta sha kama shi dumu2 yana kallonta.


               👎
Maman Twins😍


🙆Phakon Numphashi😭

        MRS SAIF


2⃣9⃣
Savoda haka yanxu ta daina xama ba hijabi,kullum xa ka tarar da ita da qaton hijabinta har qasa.

A 6angaren aunty suhaima kuwa,ita kantaa a damuwa take,don ta gane abinda sageer ke nufi akan Afif,ta rasa wa xata gayawa damuwarta.
Domin tasan duk wanda ta gayawa xai ce kawai ta koreta.

Ita kuma ta riga tayi alqawari ba xata ta6a rabuwa da Afif ba, matuqar ba gaban iyayenta ta koma va.


Yau tunda safe take shirin xuwa gidansu don jiya da daddare ake sanar da ita ummansu vata da lfy.

Dakin Afif ta shiga tana fadin"toh xan tafi sai na dawo,ke ma don kince jkn naki ba dadi ne,ai da mun je tare.

Afif dai murmushi tayi don yanxu kwata2 ba ta son shiga mutane.

Tana tafiya,Afif ta shiga aikin nata na barci.
Kamar a mafarki ta ji mutum a kusa da ita,wa xata gani❓
Sageer ne kamar wanda ya sha giya,a firgice ta diro dg kan gadon ta yi waje.
Tana wani irin kuka;sai dai tana xuwa bakin qofar sai ta ganta a qalgame.

Juyowa afirgice ta yi tana kallnsa,shi kuma ya sheqe da wata mahaukaciyar dariya yana cewa"
Yarinya baki sanni ba ne,ni nan da kike gani na riqaqqen dan bariki ne.

Dake kin xata vana nan,kamar yadda na saba idan na fita tun safe sai dare.

Afif kuka take yi sosai,tana ba shi haquri akan ya taimaka ya bude mata kofa,xata bar musu gidansu gava daya.

Sai can kuma dabara ta fado mata ta juya ciki gidan da gudu,shima sai ya bita.
Tana xuwa ta fada kitchen ta rufe qofar sannan ta fara mai da numphashi.

Yayi ta bugun kofar akan ta bude har da yi mata baraxanar xai 6alla kofar amma kememe taki.




               👎
Maman Twins😍




🙆Phakon Numphashi😭

           MRS SAIF

3⃣0⃣
Sai da aka fara kiraye2 sallar la'asar sannan ta ji ya bude kofar ya fita,a tsorace ta fito da
 niyyar yin sallah.

Tana idar da sallah juyowar da tayi sai ganinshi tayi,fuskarshi a murtuqe kmr vai ta6a dariya ba.

Bata tsaya wata2 ba,wuf tayi waje da gudu,dai-dai lkcn aunty suhaima ta sawo kanta cikin gidan.

A raxane ta riqe Afif tana fadin"lfy???
Afif dai kuka kawai take yi,ai da kunya tace"mijinta yana bibiyarta.

Tana shiga ckn gidan sai kuma tayi turus don ganin sageer a gida.
Tace"ashe har ka dawo.
Yace"eh
Tace"ya aka yi na ga afif na kuka???

Sai ya fara inda2 to.....to ya xa...a yi na sani tunda ina wurin wanka.
Aunty suhaima ta gama gane ba shi da gaskia.

Saboda hk ckn 6acn rai ta fara magana"Afiif ki gaya mun tsakani da Allah,  yayi miki wani abu ne???
Afif ta girgixa kanta,ckn tsawa A.suhaima tace"tell d truth.
Am telln u,wallahi bai mun komai ba.
Sannan ta yi ajiyar xuciya ta shige daki.




              👎
Maman Twins😍



🙆Phakon Numphashi😭


         MRS SAIF

3⃣1⃣
Tabbas dole ta dauki mataki domin ta ga abin na sageer kullam qara gaba yake yi.
Yanxu kawai xata maida Afif gurin ummanta,yaso ta riqa xuwa tana dubata.

Waya ta dauka ta kira ummanta,ta sanar da ita xata kawo yarinyar da take bata lbarinta gobe,kuma ana take so ta xauna.

Umma bata yi musu ba tace"ai taimako ne sai sun xo.

Sageer ashe duk ya ji abinda take fada"ya dau alwashin kafin ta bar gidan sai ya cika burinsa.
Tana idar da sallar isha,key kawai ta sawa kofar ta xo ta kwanta ko hijabin sallar ba ta cireba.
Don tun da ta gano halin sageer in dai xata kwanta sai ta sawa kofarta key.

Shi ma sageer ta wuri ya je ya kwanta,qarfe 12:00 dai2 ya tashi sadaf-sadaf,don tuni suhaima tayi barci.
Ya dauki key din dakin Afif ya fice.

Cikin barci ta ji kamar ana bude key,a raxane ta mqe dai2 lkcn ya qaraso cikin dakin,sannan ya kuma sa mukullin ya rufe.

Cikin xaro ido😳Afif ta fara fadin"meye hk??
Yace"ai duk rums dake gidan nan akwai extra keys a hannu na,da ke kin dauka kin sha kenan.

Ya saki wani mugun murmushi ya nufe inda take gadan2.
Da gudu ta yi baki kofar ta hau bugu da qarfin tsiya.
Da sauri ya xo yana fadin"baki da hankali ne???
Ba ki san dare ne ba.



                  👎
Maman Twins



🙆Phakon Numphashi😭


      MRS SAIF

3⃣2⃣
Bata saurare shi ba da cigaba da buga kofar.
Kamar a mafarki A.suhaima ta ji ana buga kofa,sai kuma can ta ji kamar kukan afif.
Da sauri ta nufi dakinta,tace lfy afif ki bude ni ce.

Da sauri ta dauko key dinta,ta bude
Tana shiga dakin sai tayi mutuwar tsaye,kansa tayi tana kuka tana fadin"meye hk sager ???
Mai ka xo yi dakinta da tsohon daren nan???
So kk yi ga haddasa mun ciwn xuciya,toh va ka isah ba,dama ko ancan abinda kk yi kenan??

Yau din nan sai ka bani takardata,ta juya dakinta da niyyar dauko biro da takarda.

Afif kuka take yi sosai domin abin ya girmi tunaninta.
Ga shi yanxu akan ta har aure xai mutu,dole ta bar musu gidansu.


Da gudu ta fita daga gidan,haka ta riqa gudu har sai da ta tabbatar ta yi nesa da gidan.don bata son su biyo bayanta.

Sannan ta tsaya ta fara kuka wiwi😭😭don garin yayi shiru ba ka ji motsin kowacce halitta,ga garin yayi baqi qirin don babu wuta,kusan qarfe 1:30 na dare.

Tsoro da firgici ya gama mamaya mata xuciya,kawai addu'a take Allah ya dauki ranta ta huta.


              👎
Maman Twins😍
[22:02, 07/01/2016] Umma k: 🙆Phakon Numphashi😭


Written by

               MRS SAIF

3⃣3⃣

Ta kafi qarfin 30mnts tana durqushe a gurin tana kuka,sai can kuma ta ji takun tafiya kamar ana kusanto inda take.
Kuma da alamun ba tafitar mutum daya bane,da kmr ta xauna ko ma meye ya gama da ita ta huta.

Sai kuma tayi tunani idan wani abu ya kuma faruwa da ita fa,ba lallai ta samu mutuwar cikin sauqi ba.
Kafin ta qarasa tunanin abin yi ta jiyo sautin tafiyar gab da ita.
Ba shiri ta kwashi qafafuwanta ta arta a gije.

Gudu take yi sosai irin na ceton rai,tun daga na'ibawa bata ankara va sai gata a karkasara,tana xuwa dai2 kanti bakwai ta tsaya.

Kasancewar ta ga wurin da alama xai yi mutane,don gidaje ne reras sai shaguna,ba alamar daji a gurin, tamkar dai cikin.

Baxa ido ta riqa yi tana kallon yanayin gurin,caraf idonta ya sauka a soron wani gida.
Da alama masu gidan mantawa suka yi ba su kulle gidan ba.

Ba tare da 6ata lkci va ta fada gidan,ta nemi can gefe a cikin soron ta xauna.

Wasu xafafan hawaye sk fara ambaliya a fuskartar ,wai yau ita ce da kwanan soro,rayuwa kenan juyi2.



             👎
Maman Twins😍




🙆Phakon Numphashi😭

       MRS SAIF

3⃣4⃣
A xaune take amma sam bata da nutsuwa,savoda sauron da ya mata qawanya ta ko'ina cixonta yake yi,shi yasa idonta ya bushe sam babu barci a gunta,ta rasa ma da mai xata ji da damuwar dake cin ranta,ko kuwa da sauron da ya addabeta.


Sai da aka fara kiraye2 sallar asuba sannan barci 6arawo ya saceta.

Fitowarsa kenan da niyyar xuwa masallaci ,don gabatar da sallar asuba,sai ya ji kamar ya xungiri abu.
Dai2 lkcn Afif ta farka dg rikitaccen barcin da ya dauketa.
Juyowar da xai yi sai ya ga kamar mutum,a rude ya koma cikin gidan yana fadin"hadixa!hadixa!! Fito na yi gamo.

Matar gidan ce ta fito tana ya tsine fuska tana fadin"gamo kuma tayaya???
Yace"mutum na gani a soro,kuma mu je ki gani.
Zaro ido tayi tana fadin"ni kuwa mai xai kai ni ganin aljani???
Kai dai da idonka ya gane maka sai kai ta fama.
Masallcn da bai je ba kenan yayi sallar sa a gida.

Ita kuwa Afif na jin duk abinda suke fadi,gaashi tana son shiga tace su sammata ruwan alwala,amma tana tsoron abinda xai biyo baya.


            👎
Mamam Twins😍




🙆Phakon Numphashi😭

             MRS SAIF

3⃣5⃣
Vata an kara ba,har gari yayi haske tana tunanin abin yi,daga qarshe ta daure ta cusa kanta a cikin gidan.

Sai da tayi sallama ya kai sau 5,sannan matar gidan ta fito tana waye wai???

Sai kuma ta kalleta baki bude tana fadin malam!malam!!fito ka ga wannan ce aljanar da ka ga ni ko???

A hargitse ya fito,sannan yace"tabbas ita ce.
Sai matar ta fara ja da baya tana fadin"ki fice mana daga gida ko mu qonaki da ayar Allah.

Afif ita kam abin mmki ya ke bata,ta yaya xasu ruqa manna mata abinda bata da alaqa da shi.

Cikin sanyayyiyar muryarta ta fara magana"wallahi ni ba aljana vace mutum ce kmr ku,don Allah ku taimaka ku sammun ruwan alwala na yi sallah.

Mai gidan ne ya mata kallon tsaf,sannan yace"amma baiwar Allah mai ya kawoki gidan mutane cikin dare???

Kafin afif tayi magana,matar tayi caraf tace"au kai har wani tambayarta kake yi??
To wallahi ko ba aljana bace ba xata xauna mun a gida ba.

Kai tun da kake ka ta6a ganin irin wannan halitar ido da ido,ai sai dai a TV.


             👎
Maman Twins😍




🙆Phakon Numphashi😭


          MRS SAIF

3⃣6⃣

Yanxu haka irin mugayen en matan nan ne da ake maganar sun shigo gari suna cutar da al'umar musulmi.

Afif dai roqonsu kawai take yi akan su sammata ruwa tayi sallah,mai gidan ne yace"haduza dan xuba mata ruwa tayi sallar sai ta tafi,tace"gaskia ba xata iya ba tayi gaba  ta samu acan.

Dakyar mijin ya shawo kanta ta xuba mata,a wata matacciyr buta,dama tace dg ta idar da alwalar jefer da butar xa'a yi.

Haka Afif ta riqa alwalar tana kuka,wai yau ita ke alwala da wata ru6a66iyar buta,a haka ma dakyar aka bata cikin cin xarafi da wulaqanci.

(Lallai dan adam ba a bakin komai yake ba,duk kudinka ko matsayinka lkc daya idan Allah ya ga dama sai ya sauya maka mataki.)


              👎
Maman Twins😍



🙆Phakon Numphashi😭

        MRS SAIF


3⃣7⃣
Bayan ta idar da alwalar tace da matar xa ta yi sallah.
Tace"tace tab ke kina xaton xai kaiki daki ne ki yi sallah???
Afif tace"a'a dadduma nake so.
Matar tace"toh ko a dandagaryar tsakar gidan nan vaxan bari kiyi sallah ba, bare har na baki daddumata.

Ki je can soron da kika fara xama ki yi acan,shima da kin fita xan saka a share a wanke,a tofe shi da addu'o'i domin ni kwata2 ban yarda dake va.

Afif bata kuma cewa qala va;tayi hanyar soron ta shinfida dankwalnta ta tada salla.

A daddafe ta idar da sallar savoda wani qugi da ta ji cikinta na mata saboda yunwa.

Domin yanxu saurin jin yunwa ne da ita kamar me,don aunty suhaima takanas ta ajiye mata kayan tea a dakinta,don har cikin dare tana tashi cin abinci.
Hawaye kawai taji yana bin fuskarta😭😭
Baxa ta ta6a manta aunty suhaima ba arayuwarta.

            👎
Maman Twins😍





🙆Phakon Numphashi😭

         MRS SAIF

3⃣8⃣
Bata yi aune ba ta ji qafafuwanta a cikin ruwa,don tayi saurin tashi, da gaba daya jikinta sai ya jiqe.

Yaron dake riqe da bucket da tsintsiya ta kalla,kafin tace wani abu matar gidan ta fara magna"
Ni na saka shi,na gaji da jiranki,shi yasa nace ya fara wanke gurin,idan ke va mayya vace ke fita.

Jiqaqqen dankwalinta kawai ta dauka tayi wa je tana share hawaye.
Fitowa tayi tana tafiya,ahankali sai ta ga yara na taruwa suna binta.

Nan da nan sai suka fara yawa,suna fadin"er indiya ga er indiya,wasu kuma na fadin" kai balarabiya ce.

Da kyar ta samu wani mutum ya kore su,sannan ta ja hijabinta ta rufe fuskarta,ta fara tafiya da niyyar barin unguwar.


             👎
Maman Twins😍





🙆phakon Numphashi😭


          MRS SAIF

3⃣9⃣
Aunty suhaima kuwa tana fitowa ta ga ba Afif va lbrinta,hankalnta yakai qololuwar tashi.

Gurin sageer ta koma tana kuka tana fadin"yanxu abinda kayi ya dace❓kayi adalci kena❓

Kayi sanadin da yarinya ta fita a cikin daren nan,toh ka kwana da shirin duk abinda ya sameta kai ma kana da alhaki.

Bata jira abinda xai ce va ta xira hijabinta tayi waje.
A dole shima ya xira jallabiya ya dauki key din mota ya fice.

Har ta kusa qarshen layin nasau,ya sha gabanta,yana fadin"wai ina xa ki je ne suhaima a cikin tsohon daren nan???


Cikin kuka tace"neman Afif ;bansan a wani hali take va,yarinyar tana neman taimako a halin da take ciki,ina gudun ta ta shiga mugun hannu,duniya ba gaskia yanxu.


A jiyar xuciya ya sauke,domin shi kansa yanzu ya gane kuskuren da ya tafka.
Yace"ki yi haquri mu koma gida gobe da saassafe sai mu fito nemanta.

Cikin.kuka tace"baxan iya ba idan xaka tai maka mun mu neme ta;toh idan ba hk va,kawai kai tafiyarka.

Haba suhaima kin san fa mun baro yara a gida fa.
Tace"ai gwanda su agida suke wadda ke daji fa???


               👎
Maman Twins😍





🙆Phakon Numphashi😭


        MRS SAIF


4⃣0⃣
Ba yadda ya iya,hk ya dauketa;suka yi ta yawo,amma ko mai kama da afif ba su gani va.
Sai wurin qarfe 4 suka dawo gida,tun amota aunty suhaima taci kuka har suka dawo gida.

Bayan sundawo take sanar da sageer cewa itama ba xama xata yi va,safiya na yi xata tafi gidansu.




Afif kuwa tunda ta fara tafiya wulla qafa kawai take yi,dakyar take iya tafiyar saboda axabar yunwa.

Gashi bata ga alamar xata samu abinci a kusa ba,sabo da hk ta daure ta cigava da tafiya, har axahar ta gabato amma va ta samu abinda ta sakawa cikinta ba.

Duk ta fita hayyacinta saboda yunwa,(kunsan jiin yunwa irin na mai ciki sai a hankali)

Kamar an ce ta juya sai ta hango wata mai abinci a gefe,da sauri ta nufi gurin jikinta har rawa yake.



              👎
Maman Twins😍




        MRS SAIF

4⃣1⃣
Hawaye na xuva daga idonta tace"da matar don Allah ki taimaka mun da abinci tun jiya rabona da abinci.

Mai abincin juyowa ta yi a furgice tana fadin"hava vaiwar Allah dg ganinki va ki yi kama da mai bara va,tayaya xan xuba miki abinci ina vaki daga ni har ke mu 6ata.
Gaskia baxan iya ba kinsan yanxu taimako wahala ne da shi.

Wasu hawaye masu dumi afif taji suna bin fuskarta tace"don Allah ki taimaka mun wallahi ni va muguwa bace,qaddarar rayuwace ta kawo ni wannan hali.

Mai abincin ta ga xata 6ata mata lkci akwai wasu samari a gun tace su korata kawai.
Kafin su miqe tayi sauri ta var wurin.

Tafiya take tana kuka😭😭ga ciwon da kanta ke mata tamkar xai tsinke,a hk har ta qarasa unguwar sallari,sai kuma ta ji wani irin jira na dibanta,tana neman fara amai.
Da gudu ta qarasa wani gidan bulo dake gurin ta fara yunqurin amai.
Amma ba abinda ya fito kasancwr ba komai a ckn na ta,sai wani daci2 da take ji a maqoshnta.

Yunqurin tashi tayi amma sai ta fara ganin dishi2 kanta yana juyawa;ba ta yi aune ba duhu ya mamaye mata idanu,bata ganin  komai ,nantake numphashinta ya fara qoqari daukewa.

Daga qarshe ta kifa agurin,cikinta ya daki daya dg cikin bulo2 dake gurin tuni jini ya wanke mata qafafu.

(Ni ma dai kam hannuna,ya fara ciwo savoda typing if ya dawo normal i w'll revisit u)


               👎
Maman Twins😍
[22:02, 07/01/2016] Umma k: 🙆Phakon Numphashi😭


Written by

         MRS SAIF

4⃣2⃣
Da sauri ya karaso wurin yana fadin inna lillahi wa inna ilaihi raju'un kasancewar ya hango lokacin da ta fadi.kallonta yayi sosai sai yaga kamr bata numfashi,juyawa yayi yana fadin maigida zo ka gani.

Kusn su hudu suka zo har da wani mutum daya zo siyan bulo,tun daga nesa suke salati don sun dauka ta mutu.
Sai da suka matso kusa da ita mutuminda ya zo siyan bulon ya duba ta sosai yace ai bata mutu ba da sauran numfashi a tare da ita.

Yace su dauko ta asa a motarshi ya kaita asibiti.
Kai tsaye AKTH ya wuce da ita,suna zuwa aka wuce da ita A&E.take likitoci suka rufa a kanta Allah ya taimaka tai saurin farfadowa.

Docter ne fito yn fdn ina wanda ya kawo yrnyar da aka shiga da ita yanzu.Mutumin da ya kawo ta yace gani.Docter yace su je office yana son magana dashi.


                 👎
Maman Twins😍



MRS SAIF



🙆Phakon Numphashi😭


4⃣3⃣
Suna shiga office dr yace"kai ne mijinta???
Yaca a'a ba shi bane.
Dr yace ina mijinta yake???
Mutumin gyara xama yayi sannan ya fara gaya masa yadda suka sameta ya qarashe da fadin "kaga kuwa ta yaya xan san mijinta??
Dr yace gaskiya ka kyauta don ynxu hk an samu nsrar tsaida jinin dake xuba dg jknta.

Nan da 3hrs insha'Allah ake sa ran farkowarta daga barci don an mata allurar varci.
Sai dai kafn lkcn a samamata abinci don tana tsananin buqatarsa,idan da hali ta fara shan abu mai ruwa2 kafin ta ci komai.

Mutumn yace"insha'Allah xa a kawo.
Bari na je gd na sanar kafin ta farka.
Dr yace yawwa.


Da fara'arta ta tari maigidan nata,sai dai yanayinsa yanuna mt akwai damuwa a tare da shi.
A qage ta fara tambayarsa"lfy kuwa abban islam na gan ka hk???

Hannunsa ya dora akan goshnsa sannan yace"bari ke dai nabeela wallahi wata yarnya ce.................dafe qirji tayi ta xaro ido waje,hkn da tayi shi ya tilas ta masa yin shiru.

Domn dai nabeela akwai dan banxan kishi sam bata son abinda ya hada mjnta da wt mace


               👎
Maman Twins😍




      MRS SAIF

4⃣4⃣
Don tana ms biyayya matuqa,amma da anxo xance kishi anan ne xata xama mahaukaciya tuburan.

Da ta ji yayi shiru dole ta lalubo nutsuwarta,don ko banxa tana son   jin mai ya hada su tace ina jinka mai yarnyr ta yi.

Ai na ga daga kadai nace yarinya xaki fara mun shirmen da kk saba.
Tace yi haquri don Allah mai ya faru da yarinyar???

Wata yrnya ce muka tsinceta a yashe a ckn wani hali;yanxu hk na kaita hosp.so shine nake so don Allah ki dafa mt abinci sai a hada da kayan tea nan da 2hrs nake son komawa hosp.

A xabure ta miqe tana fadin"tab!!!wallahi baxata sa6u va,ni xan dafawa wt er iska abinci???
Har kk wani samun lkci to wallahi ko xata mutu vaxan dafa va.


                👎
Maman Twins😍



🙆phakon Numphashi😭

       MRS SAIF

4⃣5⃣
Cikn mryr rarrashi yace"hava nabeela wannan fa tmkr jihadi ne kuma Allah ne xai biyaki.

Fuskrta ta juyar gefe tac"gskia ba xan iya va,ka je ka gayawa talatu ko ladidi su dafa mata alallai sai ni??

Yace"a'a tare da miqewa.
Bayan talatu ta kammala duk abinda ake buqata,yace da ita ta dauko kyn su je tare ko da xata yi wani amfani acan.

Basu fi 15mnts da xuwa va ta farka tana fadin"don Allah ku taimaka mun da abnci yumwa nk ji.

Da sauri Nuradeen ya bawa talatu umurnin ta hada mt tea,kafa kai kawai tayi sai cup suka gani.

Murmushi deen yayi sannan yace"talatu ta xuva mt abncn da sk xo da shi.


Nan da nan talatu ta xuba mata hadadden ta da kafada da ya ji hanta da kifi.
Shima dai bai kai lbri va don sai da ta cinye shi tas tayi hamdala.


A san nan ne ta qarewa gurin kallo tare da mtnen dk gurin,sannan tace"don Allah wa ya kawo ni nan???

Deen ne ya matso kusa da gadon da take ya xayyana mt duk abinda ya faru.

Tana hawaye take fadin"na gode da taimakon da ka mun.
Allah ya saka da alkhaieri.
Dr ne ya shigo yana fadin"jiki yayi kyau kenan
Deen ya amsa yace lallai kam don ga alama nan.
Dr yace"sai dai gdiar Allah,don Allah ya taimaka cikin dake jikinki bai yi komai va yana nan daram.

Dum3!!!Afif ta  xuciyarta na harbawa,ina ma ace ckn ya xube ta huta.sai km ta saki wani kuka mai tsima xuciya.


Duk wanda ke gurin yayi mmkin kkan da afif ke yi,suna tunanin ita da xa tayi farin ciki sai kuma ta fara kuka???

Dakyar deen ya rarrasheta tayi shiru,sannan ta fara tmbyrta kukan me take don ance cknta bau xube va,ko akwai wata mtsala ne????


                 👎
Maman Twins😍



     MRS SAIF

4⃣8⃣
Afif ba ta ce komai va,illah kukan da ta cigava da yi,da dai deen yaga baxa yi magana va yace"daina kukan ba sai kin gaya mn va tunda na fahimci ba kya son fada.

Yanxu ki gy mn unguwarku na je na sanarda en uwanki don su san haln da kk ciki.

Ckn kuka tace ni vani da kowa agarin nan
Ckn mmki deen yace to ina ne garinku???kuma mai kk xo yi nan garin???

Tirqashi afif ta fada a ranta don gskia ynxu ba xata kuma gywa wani sirrinta va.

Tace ni va er 9ja ba ce er qasar Oman ce,mijina ne yaci mutunci na sannan ya sake ni ya koereni va tare da ina da kudin komawa garin mu va.

Ajiyar xuciya ya sauke don har ga Allah ya yarda da mgnarta don.kana ganinta kasan bata ya kama da en 9ja va.



              👎
Maman Twins😍




      MRS SAIF
4⃣9⃣
Savoda hk yace"shike nan vari muga xuwa lkcn da xa a sallame ki sai ana nemi hanyar da xa'a turaki garinku.

Afif dai gdia kawai take xubawa.

Sai wurin 9pm suka koma gida,nabeela ta cika tayi fam don tunda suka fita ruwa ta kasa sha savoda baqin.kishi.

Yana shigowa ta fara xaxxaga ruwan bala'i,sanin hali shi yasa bai tankata va ya shige dakinsa.

Sai ta koma gurin talatu tana tmbyrta yanda aka yi.
Dama talatu akwaita da son gulma nan da nan hau gy mt qarya da gskia.
Ta qarashe mgnarta da fadin"hjia da kin ga yarinyar tab!!!ai kin sha mmki don tsabagen kyanta kmr ita tayi kanta.
Wai!!!xillaxiya kenan!!!
Shi kansa maigida idan ya kalli yarinyar sai na ga har wani rudewa yake kmr......................


Wata irin tsawa ta dokawa talatu har sai da ta diro dg kan kujera.
Cikn tsananin 6acn rai tac ke talatu ki iya bakinki.
Ta gyada kai kmr qadangaruwa tace Allah huce xuciyarki.

A ranar nabeela ba ta yi barci sosai va tunanin hnyr da xata raba deen afif kawai take.



            👎
Maman Twins😍

🙆Phakon Numphashi😭

         MRS SAIF

5⃣0⃣
Yau aka sallame Afif daga hosp.gaba daya kan deen ya kwance savoda bai samu kudin da xai tura afif qasarsu va.
Savoda ginin da yake yiwa mahaifyyarshi duk kudin hannunshi ya qare.

Gashi yana tausayn afif baya son ya kyaleta don bai san hannun da xata fada va.

Daga qarshe dai abinda yake gudu shi xai faru don dole ya kaita gidansa har xuwa lkcn da xai samu kudin,matuqar yana so ya taimaketa.


Har ta miqe xata fita dg parlorn sai kuma ta tsaya jin tsayuwar motar deen.

Sallamarta ne ya sata juyowa ckn tsananin mmki,kaitsaye idanuwanta sk hango mt wata kyakkyawar yarinya a gefen deen,dakyar ta iya saita numphashinta,tayi kukan kura ta cafko wuyan Afif tana fadin"lallai yau akwai vala'i a gidan nan.........



                👎
Maman Twins😍
[22:02, 07/01/2016] Umma k: 🙆🏻Phakon Numphashi😭

Written by

             MRS SAIF

5⃣1⃣
Cikin tsanani bacin rai deen ya fara magana"baki da hankali ne nabeela kashe er mutane xa ki yi???
Ckn tsiwa ta ba shi amsa aa gwanda na kasheta na huta,muddun xan ga mace ta ra6eka toh xan iya kashera har lahira.

Afif kuwa ko motsi ta kasa idanuwanta duk sun firfito waje don shaqar da nabeela ta yi mata bana wasa ba ne.

Da sauri deen yayi kansu ya fincike Afif daga hannun nabeela,sannan ya nuna ta yatsa yace"ki shiga hnklnki nabeela idan ba hk va xan yi mugun sa6a mk.
Kuma a gidannan xata xauna har xuwa lkcn da xan samu damar turata qasar su.
Gwanda ki yi haquri ki xauna da ita lfy tunda xaman na dan lkci ne.

Idan kk yi hk ke ma sai ki samu lada.Daga hk bai qara ce da ita komai va,yace da Afif ta taso ya nuna mt inda xata xauna.


                 👎🏻
Maman Twins😍




🙆🏻Phakon Numphashi😭


     MRS SAIF

5⃣2⃣
Gurin  talatu ya xarce da ita yace ta nuna mata dakin da xata xauna,shi xai je ya siyo mata kaya   koda dogayen riguna ne kafin ta wuce don ta samu na sawa.

Afif dai godiya take amma tana jinjina yadda xamanta xai kasance a gidan,don ta tsorata matuqa da yanda taga yanayin matar gidan.

Ba kamar yadda ta xata va ya faru domin yau kusan 8wks da zuwanta,amma nabeela kwata2 ba ruwanta da harkarta abin ya bawa afif mmki.

Shi kan sa deen ya ji dadin hkn don ya dauka nabeela ta ji nasihar da yake mata,savoda hk har ya shirya tafiyar da yake yi duk qarshn wata.Ya kan je Sokoto don gaishe da mahaifiyarshi,don babansa ya mutu tuni.

Domin yanxu hk ita yake wa gini don xai dawo da ita kano gava daya.


                 👎🏻
Maman Twins😍





🙆🏻Phakon Numphashi😭


       MRS SAIF

5⃣3⃣
Ya gama shirinsa tsaf sai tafiya,Nabeela ce riqe da jakarsa ta rakoshi sai fara'a take yi kmr wadda aka yiwa albishir da aljanna.

Deen ne yace"don Allah nabeela ki cigava da kula da Afif kmr yadda nake yi kin san mai ciki tana buqatar kulawa.

Jita yi wani mololon baqin ciki ya tsaya mata a maqoshi har sai da fuskarta ta nuna.
Yace ya dai nabeela ina magna na ji kin yi shiru.
Da sauri ta giegixa kai tana yaqe don gudun kar ya dagota.
Tace ni kaina yanxu yarinyar tausayi take bani da ban fahinceka bane sai yanxu.

Yace yawwa nabeela aqoqarta.
Tace 'Allah ya kai ka lfy.
Yace ameen tare da shigewa mota.
Tana tsaye tana daga masa hannu har ya fice dg gidan.
Sannan ta saki wani murmushin mugunta .
Sai ta shige cikin gidan da sauri.



                  👎🏻
Maman Twins😍
[22:02, 07/01/2016] Umma k: 🙆🏻Phakon Numphashi😭
5⃣8⃣
Nabeela ta gaya masa qarya da gaskiya,wai Afif guduwa tayi sai da tayi2 ta xauna taqi,har da kiran talatu shaida,itama  ta xo ta zuba qaryarta tare da shaidar xur.

Deen kam kwata2 bai yarda da xancensu ba,kullum addu'arsa Allah ya hada shi da Afif don ya taimaka mata.


3 mnths after,Afif cikinta har ya fara fitowa,duk ta rame talalace,skin din ta yayi wani yellow nd jaja2 kmr yadda farar fata yake yi idan yaxo 9ja ya ji gaashi😜😜
Duk ta wani ya mutse Allah sarki abin tausayi,kullum cikin aiki take kwata2 bata samun hutu,ga rashn sabo,duk dare da ciwon baya da ciwon mara take kwana.


                 👎🏻
Maman Twins😍



🙆🏻phakon Numphashi😭

    MRS SAIF

5⃣9⃣
Kamar kullm sun sha aiki har sun gaji,ta kona gefe tana hutawa mararta ta ji tana mata wani axababben ciwo.
Sai kawai ta ji ana kwala mata kira da kyar ta yunqura ta taashi.
Tace gani hajiaa.
Haj tace kuloli xaku fito dasu za akai  gidan abin.
Tace"toh
Tana zuwa da taga kular sai da gabanta ya fadi,va yanda ta iya adole ta cicci6i kular da niyyar dauka.
Mararta ta ji ta wani murda bayanta ya qage adole ta saki kular tayi baya tare da sakin wata qara ta fadi anan tuni jini ya wanke gurin tamkar an kunna bude famfa.

Karar da ta saki ne ya maido da hnkln sauran ma'aikatan dake gurin kanta.
Daya daga cikin su ta shiga kwalawa hajia kira,don duk sun rude ganin halin da Afif ke ciki.
Hajia kanta da ta fito sai da hankalinta ya tashi matuqa da sauri tace"wa daya daga cikin ma'aikatan ta fita ta samo mota akaita hosp.



            👎🏻
Maman Twins😍




🙆🏻Phakon Numphashi😭

    MRS SAIF

6⃣0⃣
Cikin sa'a tana fita ta samu taxi nan da nan aka daukota,aka sa amota.
Wani private hospital dake kusa dasu suka fara zuwa,suka ce gaskia vaxa su iya ba,kawai su wuce da ita AKTH don su kansu sun tsorata da yanayin da suka ga Afif.

Bayan sun isa asibitin doctors suka rufu akanta,don tayi  miscarriage nemai tsanani,da taimakon Allah likitan ya samu nasarar kwaashe mata ragowar 6arin da tayi ta hanyar yi mata wankin ciki.

Amma kam Afif ta sha axaba ba kadan ba😰😰don har yanxu jikin nata sai a hankali.

Don likitan da yake dubata ya sanar da ita cewa sai nan da 2wks xa'a sallameta.
Sai dai farin cikinta daya da dr ya tabbatar mata da cikin jikinta ya xube.Don hk ta yi farin ciki ta miqa godiyarta ga Allah da ya yaye mata daya daga cikin damuwarta.


Yanxu babbar damuwarta shine hajia ta juya mata baya tace"ta gaji da kashe kudinta a asibiti,ga shi dr yace sai nan da 2wks xa'a sallameta.

Wasu zafafan hawaye ta ji suna bin fuskarta.
Daga hannayenta sama tayi tana addu'a
Tana cewa"ya Allah ka ga halin da nake ciki ya ubangijin talikai ya Allah ka kawo mun dauki ka kawo mun mafita mafi alkhairi a tare da ni YA ALLAH!!!
Sannan ta runtse idonta ragowar hawayen da ya cika mata ido ya samu damar gangarowa.😭😭




                👎🏻
Maman Twins😍
[22:02, 07/01/2016] Umma k: 🙆🏻Phakob Numphashi😭

Written by

MRS SAIF

54***

Afif ce a xaune tana cin abinci,domn yanxu hankalnta ya dan kwanta don deen yana iya qoqarunsa akanta.

Musammn yake xuwa ya tambayi mai take buqata,data fada nan da nan yakw sawa akawo mata.

Hannu ta daga da niyyar kai loma bakinta,sai ta ji an kwa6e hannun abincn ya xube qasa.

Daga kanta ta yi don gani waye,Nabeela ta gani da wuqa a hannunta tsirara sai walwali take.

Gava daya hankalin Afif ya taashi;cikin rawar murya tace"aunty nabeela lfy???

Tsawa ta daka mata tace waye auntyn taki???
Kar ki kuma kirana da aunty.



             
Maman Twins




Phakon Numphashi

MRS SAIF
55**

Nabeela ta cigaba da fadin ki nutsu,ki saurari abinda xan fada miki.
Cikin biyu dole ki xa6i daya:
Ko ki bar min gidana ko kuma ki rasa ranki wanne kk so???

Jiki na rawa Afif tace xan bar miki gidanki yanxun nan.
Murmushi nabeela tayi tare da fadin miqe ki fita,yanda kk shigo hk xa ki fita,don va abinda kk zo da shi.

Dama Afif ba ta yi niyyar daukar komai ba hijabinta kawai ta saka sai takalmi tayi wa je tana xubar da hawayen baqin ciki.

Tana tunanin ina ta nufa kuma,wanne wacce irin rayuwa ce❓wani kuka mai sauti ya qwace matata cigava da rerawa.

A bakin gate din gidan suka hadu da ladidi tana dawowa daga aikin da nabeela ta yi mata.

Bayan ta shiga gidan take tambayar nabeela lafiya ta ga Afif ta fita kuma tana kuka???

Nabeela tace"korarta na yi,kuma saura idan ya dawo ki gaya masa,ke idan ma na ji maganar nan a bakin wani toh nasan ke kika fada,kuma ki tabbatar da qarshen xaman ki ya xo a gidan nan.

Ladidi ta qwalalo ido waje tana fadin"ba dai a baki na va kuwa.
Dama ni yarinyar haushi take bani.

Afuwan kwana biyu kun ji ni shiru avuvuwn ne sai aslow,buh Insha'Allah gobe ma zaku ganni.



         
Maman Twins
Phakon Numphashi

Written by

        MRS SAIF

56***

Bayan fitar Afif daga gidan tayi ta watan garari a gari,don.neman wajen xama amma duk inda ta je sai ayi ta gudunta.
Idan abu ya hadata da namiji sai ya nemi ya kawo mata maganar banxa.

Dakyar ta samu wata mata ta hadata da wata hajia mai gidan abinci a unguwar gandun albasa.

Bayan matar ta gabatar da Afif a gurin haj.sai hajiyar tace "xan kar6eki xan riqa baki abinci da sha da kuma wurin kwana,shine ladan aikinki.

Domin ina da masu aiki da yawa xuwa suke yi suna tafiya,su ina biyan su,amma wadanda basu da galihu kmr ke bana biyansu ko ficika.
Domn ni na taimaka musu da muhalli hadi da ci da sha.

Afif girgixa kai tayi hawaye na xuva daga idonta tace"ta yarda.wai yau ita ake kira da marar galihu hmm rayuwa kenan.


           
Maman Twins




Phakon Numphashi

MRS SAIF

57***

Hajiya ce ta katse mata tunani ta hanyar cewa"amma daga ganinki ba kiyi kama da en qasar nan ba.
Afif tac eh ni ba erqasan nan bace.
Nan dai ta gayawa haj. Lbrinta kmr yadda ta gayawa deen.
Hajiya tace Allah ya kyauta.
Bayan deen ya dawo bai tarar da Afif ba,nabeela ta gaya ms qarya da gaskia.

Fakon Numfashi

Written by

            MRS SAIF

61***

Qarfe 4pm agwogon 9ja cikin jahar kano,Adai2 lkcn mutane ke xarya acikin asibitin AKTH don alkcn aka vada damar fara xiyarar marasa lfy.

Deen ne da Nabeela suka biyo ayarin en dubiyar,sun xo duba matar abokin deen,ga shi sun rasa wurin da aka ce matar take.
Saboda hk tafiya kawai suke suna raba ido,ko da Allah xai saka su gane gurin da take.
Domin yayi ta kiran wayar abokin nasa taqi shiga.

Sun so dai2 labour room,Nabeela ta ga wata qawarta tace"da deen bari mu gaisa ina xuwa.
Bata jira abinda xai ce ba tayi gaba abinta.
Yafi qarfin 10mnts yana jiranta amma ko kallon inda yake ba ta yi,hirarta kawai take yi hankali kwance.



           
Maman Twins




🏻Phakon Numphashi

     MRS SAIF

62***

Da ya ga hk sai ya yanke shawarar shiga postnatal ko xai dace da ganinta acan.
Yaxo daidai room5 kasancewa qofar dakin a budetake.
Karaf idonsa ya sauka kan Afif tana tsiyayar da hawayen da ya xame mata aboki.
Murxa idonsa yayi don ya tabbatar da gaske ne ko kuma idonsa ne.

Don ya ga kamar kama ce kawai,domin Afif ta fi wannan kyan gani.
Amma duk da hk bai yi qasa a gwiwa va,qarasawa yayi daf da gadonta yayi mata sallama.

A hanxar ce ta dago da fuskarta don ko bata kalleshi ba,ba xata manta mai murya ba.
Yanayin kallon da take masa shi ya tabbatar masa da Afif ce.

Qara matsawa in da take yayi yace"Afif
Sai da tayi qoqarin goge hawayen fuskarta sannan tace"na'am.
Deen yace baki da lfy ne???
Na ganki a asibiti??
Daga kai tayi alamar eh.
Yace mai ya sameki???
Bata iya ce da shi.komai ba sai kuka da ta cigaba da yi.

Yace don Allah ki daina kukan nan ki yi mun bayani.
Kuma mai yasa kk gudo daga gidana.???
Tace ba komai.
Yace da gaske guduwar kk yi kenan❓


         
Maman Twins




    MRS SAIF


63***

Tace"a'a
Yace"toh ina so ki gaya mun duk abinda ya faru dake tun dg barinki gidana har kawo yau.

Cikin kuka ta xayyanawa deen duk abinda ya faru har xuwa xamanta gun hajia mai abinci.

Deen ransa yayi matuqar 6aci akan abinda nabeela ta yi.
A wanni 6angaren kuma tausayn Afif ne fal xuciyarsa.
 Yana cikin tunani abin yi nabeela ta kira shi wai tana ta jiransa tun daxu bata ga inda yayi ba.
Ransa a 6ace yake ce da ita ta jira shi anan inda ya barta xai fito su tafi.
Afif kallonsa kawai take tana aikin kukan da ta saba.
Yace"please Afif stop cryn wai ke ba kya gajiya da kuka ne???

Yace kince nan da 2wks xa'a sallameki ko???
Gyada kai kawai tayi alamar aa.
Yace Insha'Allah b4 lkcn xan san yadda xa'a yi ki koma gida.

Cikin rashin fahimta abin da ya fada,
 tace"yaya deen wallahi i will never return 2 ur home.
Murmushi deen yayi yace"l mean Oman not my home.
Afif ba ta san lkcn da ta tintsire da dariya ba.

Abin har ya bawa deen mamaki yana ta kallonta.
Yace da ita dama kina dariya haka



         
Maman Twins




        MRS SAIF

65***

Tace"sosai ma kuwa,quncin rayuwa ne kawai ya chanxa ni.
Yace ok,Ni zan wuce sai dai Insha'Allah xan riqa xuwa dubaki b4 sallama.
Tace"toh na gode yaya deen Allah ya saka da Alkhairi.
Yace'ameen.

Bayan sun hadu da nabeela,tana son yi masa qorafi akan dadewar da yayi,amma yanayinsa kawai ta kallah ta kama kanta.

Daga qarshe ma cewa yayi su koma gida wata rana sa dawo don lkcn dubiyar ya kusa wucewa.

Don yayi alqawarin va xai kuma yi mata xance Afif ba,komai xai gabatar da abinsa ba tare da ta sani va.

Yau aka sallami afif daga asibiti,tun da sassafe deen yake shige da fice don ganin komai ya ta fi kmr yadda ya tsara.
Allah ya taimake shi komai ya xama ready,so direct hosp.ya wuce ya dauki Afif sai airport dama shi take jira don tun 10am aka bata sallama.

Afif kam murna ce fal cknta don ynzu ta fi mararin qasar haihuwan ummynta akan qasarta,don 9ja kwata2 ta fitar mata arai.

Deen kuwa ya sha addu'a a bakin Afif har sai da yace ya isah.
Qarfe jirginsu Afif ya daga sai qasar Oman.




         
Maman Twins
[22:03, 07/01/2016] Umma k: 🏻Phakon Numphashi

Written by

       
MRS SAIF

66**

Bayan sun isa qasar kaitsaye Afif taxi ta samu xuwa unguwr kakanninta.
Tana shiga gidan ya hade da ihun murna kmr xa a hadiyeta don so.
Sai dai sun sha mamakin ganin yadda ta koma,duk da cewa suna da lbarin duk abinda ya faru.
Don takanas Abu Athim da ummu Athim (kakannin afif)suka je 9ja akan maganar don kuwa Aby ya sha fada ba kadan va.
Suka ce"mai yasa bai turo musu ita ba,idan shi baya sonta to su suna sonta a hk.
Tun lkcn da suka dawo ummu athim ke rashn lfy yau ciwo gobe lfy.Domin tana tsanani qaunar Afif.


Afif na shiga wurin ummu athim da sauri ta taho ta rungumeta tana kuka ta fara cewa ina kk shiga ya sanyin idaniyata muna ta nemanki a 9ja ba mu sameki va,hk muka dawo ckn qunci da baqin ck.
Afif itama cikin kukan take cewa jaddy magana ce mai tsawo bari na huta sai na gaya miki duk abinda ya faru.(Duk maganar da suke ackn harshn larabci suke yi)


           
Maman Twins



Phakon Numphashi

              MRS SAIF

67***

Bayn ta hutah tayi wanka ta ci abinci,alkn abu athim ya dawo da sauran en uwan ummyn afif,duk sun hallara a parlor Afif ta shiga xayyana musu yadda rayuwa ta kasance mata tun daga lkcn da Aby ya koreta har kawo yau.

Allah sarki kakanninta kam kuka suke yi sosai don tausayn er jikarta su,ummu athim ta qara rungume Afif tana cewa da yardar Allah daga yau kukanki ya qare don baxa ki  koma 9ja ba kwata2.

Afif kam murmushi ta yi don ko ita idan xa ta samu ganin ummynta wa Abynta nd her brothers a duk lkcn da take so,ita kam va sai ta xauna a 9ja ba,domin ta fice mata a rai.

Babban abinda ke damunta don tun faruwa al'amarin da shi take kwana da shi take tashi shine da wace fuska Aufiq xai dauki avun da ya faru❓shin xai dauki qaddara ne ko kuma xai gujeta shima❓wannan tamvayoyin su suke mata yawo a xuciya duk tsawon lkcn da ta dauka ba sa tare.
Don dai tana tsananin son Aufiq sai dai shi bata san matsayinta a gunshi va yanxu.

Wasu hawaye ta ji sun gangaro akan fuskarta,tabbas duk wanda yayi sanadiyyr ruguxa farin cikin rayuwarta ba xa ta ta6a yafe masa.


             
Maman Twins




                MRS SAIF



68***

A 9ja kuwa,kuma ckn garin Abuja,Aby ne akwanci a dakinsa duk abun dunia ya dame shi don tun faruwar al'amarin bai ta6a shiga tsananin nadama ba irin yanxu da yasan gaskiar abinda ya faru.

Wasa-wasa abin har ya xame masa ciwo,don ya bayar da sanarwa a News Media amma shiru ba alamar xa a ganta.
Tun ana yi iya Abuja har ya xama d whole country yi ake yi,duk News Media na 9ja duk inda ka kama abu daya dai shi ake yi wato sanarwar 6atan 'yar Senate President wato Afif Nasir Mai Nasara(don yanxu shine akan kujerar.)

Har da maqudan kudi Aby ya saka tukwaici ga duk wanda ya ganta.(abinda bai sa ni va tuni Afif ta yiwa 9ja kwara)



           
Maman Twins



              MRS SAIF
69**

Ummy kam yau ta tashi da tsananin farin ciki da tun tafiyar Afif ta kasa samu,domn sun yi waya da iyayenta sun sanar da ita afif na gurinsu,sai dai sun ja kunnenta akan kada ta kuskura ta sanar da Aby.
Tace ita kanta ba ta da niyyar gaya ms ta fi son ya qara dandanan irin axabar da ta sha na rashn afif.

2mnth kenan da komawar Afif Oman,ta yi kyau abinta har da er qiba ta yi kmr ba ita ce ta yi wannan kojalewar nan va.
Toh ba dole ba;ana kula da ita sosai ko tari tayi sai an tambayi mai take so.
Damuwarta daya Aufiq amma ta qudiri niyyar tmbayar jaddy yau domin ba xata rasa sanin wani abu ba.

Murmushi jaddy ta yi tace"ai na dauka kin manta da Aufiq shi yasa ban miki xancensa ba.

Ta cigava da fadin"Aufiq ya ji abin da ya faru dake amma kwata2 bai yarda ba don kuka ya riqa yi sai kace qaramin yaro yana cewa wai sharri akai miki yasan vaxa ki aikata abinda aka ce ba.
Kmr fa ya xautu hk ya koma,kullum yana zarya hanyar 9ja wai ko xai ganki.
 

           
Maman Twins



                MRS SAIF

70
Daga qarshe sai da aka dage da addu'a kansa Allah ya taimaka ya dawo dai2.
Yanxu hk Abynsa ya tura shi qasar Paris don yana shirye2 bude wani company acan,kuma shi ya dorawa alhakin kula da komai.
Amma ya dade da tafiya nan va dadewa va xaki kanshi ya dawo.
Wasu siraren hawaye afif ta ji sun xubo mata,wanda ta kasa tantance na farin ciki ne ko kuma na tausayn hubbynta.


Aby dai jiki yayi tsanani don har yakai ga kwanciya hosp.Ummy ynxu kam tausayinsa take ji don dr yasanar da ita daf yake da kamuwa da ciwon xuciya.
Saboda hk ta yanke shawarar tuntu6ar iyayenta don su bata damar sanar da shi halin da ake ciki.
Basu yi musu va,suka ce ta gaya ms don sun girgixa da halin da aka ce ya shiga.

Aby ba qaramin farin ciki yayi ba,da ya ji cewa Afif na qarqashin kulawar kakanninta
Sai ya ji gaba daya ya warke.

Bayan 5dys aka sallame shi daga hosp.nan da nan ya shirya tafiya qasar Oman.
Su yaya Thauban,Thabit,Sabir,Abid duk sun hallara domin da su xa'a ya tafiyar.



             
Maman Twins
Phakon Numphashi

Written by

            MRS SAIF

76
Kabeer ya cigaba da fadin"afif na kwashe tsawn lkc ina bibiyar rayuwarki don na samu mkmncyar rana irin wadda na samu.
Wadda ya kai ni ga duk wani motsinki na san da shi.
Idan ba ki manta ba akwai lkcn da na je mkrntr ku ina kyrwa to shine silar faruwar komai.

Wata rana xa a yi daurin auren daya daga ckn malamn mkrntr a garin katsina,mafiyawancn mlmai sun je har da shugaban mkrntr.

Ba mu fi 5 ba a mlmai wadanda ba su je ba.
Kwatsam ana ckn krtu akace mlmn da suka je daurin aure sun yi mummunan  hadari duk sun mutu.

Akace wasu sai da aka riqa kankaro namansu dg jikin mota.


         
Maman Twins




77
Nan da nan mkrnta ta hargitse da koke2 ba shiri aka sallami dalibai,malamai ma kowa ya tafi.
Ina xaune ina jiran fitowarki don kullm sai kin wuce nk tafiya.
Shiru2 ba ki fito ba,hkn ya tilasta mn komawa ckn mkrntar na gani ko lfy?,?,?

Ina shiga direct class dinku na wuce,Ayashe na tarar dake kin fadi kmr ba kya numfashi sai da na yi naxarinki sosai na gane kina yi sai dai hankalinki baya jikinki.

Nantake shaidan ya qara qawata mun surar jikinki,yayi ta ingixa ni ya namun mummunar hudu va.
Va tare da 6ata lkci ba na cika burina akanki af..............kuka ne ya kwace ms mai cike da tsantsar nadama.
Bayan nan na je nace da masu gadi ga ki can kin fadi su xo su taimaka a fito dake.
Abin mmki muna xuwa sai mk tarar kintashi.
Dakyar kk iya miqewa ku fito bakin gate.

Ckn sa'a muna fitowa drivernki ya xo kk tafi.



         
Maman Twins



         MRS SAIF

Afif kuka take kmr ranta xai fita ta kuma qanqame ummy tana cewa"ummy kin tuna lkcn da na dawo dg sch.kika tmbaye lfy kin ganni wani iri nace bani da lfy kin tuna.
Ummy tace a,afif ta cigaba da fadin
Alkcn na dauka period nake har na daina sallah sai daga baya na yi wanka na cigaba da sallah.
Ummy tana dan bubbuga bayan afif alamar rarrashi tace duk na gane afif kiyi haquri hk Allah ya tsara miki.


           
Maman Twins
[22:03, 07/01/2016] Umma k: Phakon Numphashi


Written by

            MRS SAIF


Ckn kuka kabeer yace Afif don girman Allah ki yafe mun,idan har ba ki yafe mun ba na je lahira ban san yadda xata kasance mun va.
Kalli yanda na xama duk akan haqqinki mun je qasashe kala2 an kashe maqudan kudi don duk na samu lfy amma a banxa.

Don hk na yanke shawarar gaya miki kuma na nemi gafararki don na gane haqqin ki ne ke dawainiya dani.

Afif vata ce komai va illa sharar hawayen fuskarta,
Daddyn kabeer ne ya tashi ya je har inda take yace"Afif don Allah ki yafe wa dana ya gane kuskuren da ya tafka kuma ya ga sakamakon abinda ya aikata.
Don girman Allah ki yafe ms.Takanas na ajiye ayyukana na biyo shi don neman gafararki don Allah ki yafe masa.

Afif baxa ta jure ganin babban mutum kmr sa yana mt magiya hk ba,saboda hk tace ta yafe masa.


 
         
Maman Twins

Aufiq ya dawo ya ji lbarin afif na qasar,murna kmr ya taka dan jariri,ko hutawa bai yi va,sai ga shi agidansu Afif.

Da ta fito kmr ya hadiyeta don so,don gani yayi ta qara kyau fiye da da.
Yake tmbyrta da gaske ne abinda aka gy masa ya faru tace"gaskia ne nan take ta gy ms duk abinda ya faru.....................
Aufiq ya tausayawa Afif sosai sai dai ya mt alqawarin kasancewa tare da ita har abada.
Shi da ita mutu ka raba,domn so na haqiqa yake mata mara algus son gskia kuma son Allah.

Kafin su bar qasar sai da aka kira ingantattun malamai suka yiwa Afif ruqiya aljanun jknta suka fita.
Sannan aka sa ranar bikinsu.



         MRS SAIF

Suna komawa 9ja Aby ya shirya xuwa kano domn yace yana so ya gana da su yaya deen da Aunty suhaima kafin biki.

Motoci sun kai 10 hadaddu kuma tsadaddu wadanda duniya ke yayi suka dau hanyar garin kano.

Direct gidan aunty suhaima suka nufa,suna shirin fita ita da sageer(don tuni sun  dai2 ta dan ya gyara halinsa)
Sai sk ga motoci na parkn qofar gidansu gaba daya sun tsorata dan daga ganin motocn kasan manyan qasa ne aciki.


         
Maman Twins



Fitowa suka riqa yi 1 by 1,har aka xo kan Afif da gudu Aunty suhaima taje ta rungumeta tana kkn dadi.
Sageer kuwa kunya kmr ya nutse duk wanda ke gurin sai da ya lura da halinda ya shiga.
Aby yace ya saki jknsa ya manta da abinda ya faru ya riga ya shige.
Anan ya nemi afuwar afif ta kuma yafe masa.

Aby ya rubatawa aunty suhuaima cheque na 3mllion yace asiyawa su bilal swt.(ka ji mnya)
Ummy wata danqareriyar sarqar gold ta kawo mata xata kai 1.5mllion tare da I.V na bikin Afif.

Aunty suhaima sai gdia take tare da alqawarin xa ta xo bkn.
Daga nan gidan deen sk wuce,ba su tarar da shi va sai nabeela.
Nabeela kam rudewa tayi ta diririce ta shiga borin kunya wai dama neman afif take ta bata haquri.

Ummy tace komai ya wuce kawai dai ko nan gaba kada ta kuma wulaqanta dan Adam,don Allah da kansa ya karrama shi.kuma ga aya nan kin gani akan afif don nasan xuwa ynxu kin fahimci waye ita.

Nabeela ta durqushe anan ta neman gafarar afif.
Afif tace ta yafe mt.
Ana ckn hk sai ga Deen ya dawo,bayan sun gaisa yake tmbyr afif mai yasa tata fi oman bayan iyayenta suna ta nemanta.
Anan dai aka warware ms duk abinda ya faru.

Shima yaya deen Aby ya ms yayyafn naira  don cheque na 10mllion wai ya qara a ginin da yakewa mahaifiyarsa.
Yace kuma duk.lkcn da yake da wata buqata ya sanar da shi.

Allah sarki deen yana ta godia tare da alqawarin xuwa daurin auren.
Nabeela kam sai hawayen nadama take xubarwa.Rayuwa kenan.
Hk suka riqa bin wuraren da Afif ta xauna suna musu yayyafun kudi har gurin hjia mai abinci sai da suka je.



             MRS SAIF
A yau saturday dubun dubatar al'umma dg sassa na duniya suka shaida daurin auren AUFIQ & AFIF wanda shugaban qasar 9ja ya kasance waliyan amarya,shugaban qasar Oman ya kasance waliyin ango wanda aka daura a central mosque dake Abuja.
Tsayawa fadar taron jama'ar da wannan daurin auren ya tara 6ata lkci ne.
Hk an yi events dff types,lyk Arabian events,indian nd namu na hausa.

Daga qarshe ummy ta hada mata qayatacciyr walima,inda xa'a yi using red & black wato a matsayn dress code din walimar.

Wasu hadaddun arabian gowns aka raba kyauta ga duk wanda ya samu arxiqin
Xuwa gurin. Suma red and black.

(Nima sai da na shiga na fita na samu damar kar6awa writters don tun da aka fara bikin da mu ake yi)

Imam's Family ma ba abar su a baya ba don suma na samu nasarar kar6a musu nasu ankon don hk kowa xai je.

Guri ya sha decoration ba a magana,don amarya kadai ta isa ta qawata gurin.don fadar kyan da tayi ba abune mai sauqi va.
Don duk wanda ya kalleta sai dai ka ji yana tasbihi ga ubangijin da ya qagi kyakkyawar halitta irinta Afif.



           
Maman Twins
[22:03, 07/01/2016] Umma k: 🏻 Phakon Numphashi

Written by

           MRS SAIF



WOW❗ka ga writters kayan kmr don su aka yi,kun san su ba dai iya daukan wanka ba.

Malamai da damna sun ba je kolin baserarsu don ganin sun fahimtar da amarya haqiqanin abinda aure ya qunsa.
An wa'axantu domin duk wanda ya je walimar ya qaru.

Daga nan malama Fateema(FAI) ta nemi a bata damar gabatar da lecture mai taken ILLAR SAKA BATSA A NOVEL.
Don ganin yadda writters suka cika gurin kmr ana bikin daya dg cikin marubuta.
Domn ta dade tana neman irin wannan damar bata samu va,sai yau.


Ta fara maganarta kmr haka"
Assalamu alaikum en uwana writters 1st of ol ina so na jinjina muku abisa qoqarin da kuke yi na rubutu,musammn authors on social media tunda babu wani benefits da kk samu,amma duk da hk kuke dagewa kuna shan wahalar typin,sai dai muce Allah ya saka mana da alkhairi.

              👎🏻
Maman Twins😍



Amma abinda yake matuqar damu kai har da wasu dg cikn al'umma shine yanda wasu daga cikin Writters ke xagewa su rubutq batsa son ransu
Ko kunya basa ji.
Sun manta da duk abin da suke yi Allah yana jinsu yana ganinsu.

Kuma wannan rubutun da muke gani ba wani abu ba,toh wallahi tsaf xai kai mutum cikin wuta.
En uwana mu yiwa kanmu karatun ta nutsu domn rayuwar duniya dan lkci ne qanqani da aka ba mu don mu gina lahirar mu a ciki,idan kk biyewa rudun shaidan sai ya kaiki ya baro.

Sukan su wasu daga cikin readers sun fison buks da ake maganganun batsa a ciki,sai ki ga an fi rubibinsu anfi son karatunsu.

Saboda hk kar ki damu da irin wadannan domn a ckn su babu wanda xai tayaki kwanciyar qabari,only u nd ur deeds.

Wallahi akwai wani post da na gani yayi bala'in sosa mn xuciya.
Matar da tayi post din tace"don Allah adaina rubuta numberta a buk,domn an samu wasu buks idan an gama daga qarshe sai a saka numberta,kuma ga shi matar aure,sai ai ta kiranta har da maxa.
Wani da ya kirata wai sai yace gskia ta burgeshi domin ta iya luv idan yana karantawa har releasn yake ku ji fa en uwana wannan abun kaico ne ga duk xuciya mai imani.

Haba er uwa ke kuwa mai yayi miki xafi,kina nan kin saki baki wai ke kina writtn novel,Ashe ba ki san kina nan kina saka garada wani yanayi tare da diban kwando-kwando na xunubai.
Ko fa xina mutum ya aikaita a dalilin karatun novel dinki,kema fa kina da kaso a ciki domin ke ce sila.
Daga qarshe ina yiwa marubutanmu fatan alkhairi,Allah ya qara baseera da haxaqa,Allah kuma yasa mu gyra.👏🏻👏🏻
Er uwarku(ustaxiyar marubuta)

(Nima dai kam maman twins jikina yayi sanyi da yawan writters na ga jikinsu duk ya mutu,kun san mu akwai jin wa'axi.

Daga qarshe an ci an sha an yi brush da naman dawisu,an yi kuma guxuri, Aka watse kowa ckn farin ck da annushuwa.




            MRS SAIF

Ranar sunday aka dauki amarya 4rm 9ja 2 norway(domin can Aufiq ke aiki)
Soyayyrsu suke yi  mai tsaafta da tsantsar qaunar juna,ko motsi Afif tayi sai Aufiq yace mai kike so ne Qalbeenah.

2yrs after,Afif ta haifi 'yarta mai suna Nasreen kyakkyawa tamkar an tsaga kara ita da Afif.
Saboda hk suka yi alqawarin kula da yarinyar bisa tafarkin addini.
Don sun ce idan Allah ya nuna ms girman yarinyar indai xata shiga mutane dole ta riqa 6oye kyanta ta hanyar sa liqab don kaucewa fadawa irin halin da Afif ta tsnci kanta a ciki.

Nasreen ce tashigo da er tafiyarta ta en koyo,saura qiris ta fadi Afif da Aufiq suka tashi da gudu su kai wurinta a tare suka dora hannu akan yarinyar sk dagota sai kuma suka rungumeta tare da sakin wani murmushi mai qayatarwa.


   Tammat Bihamdulillah

Anan na xo qarshen wannan buk,fatan dai Allah ya sa saqon da nake son isarwa ya je gurin da ake son ya je,domn akwai abubuwan lura a littafn PHAKON NUMPHASHI Kamar hk:
llar korar yara wanda qaddarar rayuwa ta afka musu kmr afif,domin wasu ta wannan hanyar ne suke xama karuwai,su je sai ta haifar shegu suma shegun idan sun tashi sbd rashn cikakkiyar tarbiya da kulawa sai suma su tsumduma irin harka,daga nan sai a samu gurbatacciyar al'umma.

Ilar tsananin kyau domin kyau kowa na son shi amma idan yayi yawa yana xama musiba,musmmn ba abi da shi ta hanyar da shari'a ta amince va
Domn irin su Afif ne shari'a ta bawa damar saka liqab bayan sun suturce dukkan jikinsu domn gudun afkuwar fitina a ban qasa.

Allah ya yafe mana kurakuran da muka yi,abisa rashin sani ko kuma ajixanci irin na dan Adam.


   SPECIAL THNX 2
➖Members ofHausa Novel's Writters.

➖Members of my grp(ECLUSIVE LADIES)

➖My Fans a duk inda suke luv u ol
➖Nd mrym KB & mrym mashi.
Aysha A Bello(6ingel)
Khadija Umar kura.....


       DEDICATED 2
-Amaryar gobe sis Mrym A Imam(Allah ya sa ayi lfy a gama lfy ya kuma ba da xaman lfy ameen


             URS
Fatima A Imam (MRS SAIF)
           KUMA
Maman Twins

Sai mun hadu @my next novel Ahlul Kitab📚

6 comments:

  1. RUGUNTSUMI 1 2 & 3


    http://gidanlabarai.blogspot.com/2017/01/ruguntsumi.html?m=1

    ReplyDelete
  2. Gaskiya wannan labari ya kayatar kuma akwai fada karwa musamman ga iyaye, da kuma muhimmancin girmama dan adam.

    ReplyDelete
  3. Wow gaskiya wannan littafin yana da dadi sosai mun gode


    https://mynovels.com.ng/jiki-na-yake-so-complete-hausa-novel/

    ReplyDelete
  4. CASINO RULES AT JACKSON BUILDINGS in Biloxi, MS - JTAH
    With 15 acres 제주도 출장샵 of tropical trees, JTR Hotels & Resorts Casino is located in Biloxi, MS. 상주 출장샵 It is 계룡 출장샵 one of the finest destinations for 김해 출장샵 entertainment. 서울특별 출장안마

    ReplyDelete